Isa ga babban shafi
HRW

Ana azabtar da yara a yaki da ta'addanci- HRW

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Human Rights Watch ta yi zargin cewa, ana ci gaba da tsare kananan yara tare da azabtar da su sakamakon matakan tsaron da jami’ai ke dauka wajen yaki da masu tsattsauran ra’ayi na kungiyar IS a Iraqi da Syria da kuma Boko Haram a Najeriya.

Jami'an tsaro na azabtar da yara a yaki da ta'addanci da suke yi a Iraqi da Syria da Najeriya da Afghanistan da Isra'ila- HRW
Jami'an tsaro na azabtar da yara a yaki da ta'addanci da suke yi a Iraqi da Syria da Najeriya da Afghanistan da Isra'ila- HRW Reuters/路透社
Talla

Rahotan da kungiyar ta fitar a yau, ya nuna yadda ake ci gaba da tsare kananan yara a kasashe 6 da ke fama da tashe-tashen hankula da suka hada da Afghanistan da Jamhuriyar Demokiradiyar Congo da Iraqi da Isra'ila da yankin Falasdinu da Najeriya da kuma Syria.

Jo Becker, daraktan kare muradun yara na kungiyar Human Right Watch ya ce, gwamnatoci na tsare kananan yara na dogon lokaci ba tare da mika su a kotu ba, kuma ya ce, ana tsare da yara dubu 1 da 433 a Syria kadai, yayin da aka sake 436 daga cikin su.

Mr. Becker ya  kara da cewa a Najeriya kuwa,  ana tsare da yara 120 a barikin Giwa kuma wasu daga cikin su da ke da shekaru kasa da 6, sun kwashe shekaru a hannun jami'an tsaro.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.