Bahamas ta gargadi ‘yan kasarta zuwa Amurka
Gwamnatin kasar Bahamas ta yi gargadi ga ‘Yan kasarta su yi hankali da rayuwarsu a yayin da suke shirin zuwa Amurka saboda matsalar wariyar launin Fata da 'Yan Sanda fararen fata ke harbe bakake.
Wallafawa ranar:
Yawancin dai mutanen Bahamas Bakaken fata ne, kuma tashin hankalin da ake yi a Amurka barazana ne ga rayuwarsu.
Ma’aikatar harakokin wajen Bahamas da ta fitar da gargadin tace ‘yan kasar su yi taka-tsan tsan ga duk wata mu’amula da ta hada su da ‘Yan sandan Amurka.
Gobe litinin dai ranar hutu ce a Bahamas kuma ana tunanin ‘yan kasar za su yi amfani da dogon hutun domin zuwa Amurka.
Rikici dai na neman kazancewa a Amurka sakamakon harbe wasu bakaken fata da ‘Yan sanda fararen fata suka yi .
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu