Isa ga babban shafi
Brazil- WHO

Kungiyar Lafiya Ta Duniya Ba Za Ta Kwace Gasan Olympics Daga Brazil Ba

Kungiyar Lafiya ta Duniya , WHO a takaice ta kawar da dukkan wani shakku cewa za'a zakuda da gasan wasannin Olympics daga birnin Rio De Janairo na kasar Brazil zuwa wani wajen saboda cutar nan dake sauya halittan jira-jirai da ake kira Zika.

Shugaban riko na kasar Braz Michel Temer
Shugaban riko na kasar Braz Michel Temer Reuters/路透社
Talla

Wasu masana 150, da suka kunshi manyan likitoci da masu bincike da wasu kwararru ta fannin kiwon lafiya, ranar Juma'a data gabata, suka rubutawa kungiyar Lafiya ta Duniya, wata wasika dake bukatar a zakuda da gasan, ko kuma a jinkirta saboda annobar cutar Zika.

Suna masu cewa gudanar da gasan a birnin Rio De Janairo, gari na biyu da cutar ta yiwa illa, ganganci ne sosai.

Amma kuma Kungiyar Lafiya ta duniya tace zakudawa da gasan babu wani alfanu.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.