Isa ga babban shafi
MDD- Burundi

MDD ta damu da halin da Burundi ke ciki

Majalisar dinkin duniya ta nuna matukar damuwa game da halin da kasar Burundi ke ciki da yadda ake kama mutane ana tsare su, da kuma yadda kasar Uganda da ke makwabtaka da ita ke koran ‘yan gudun hijira daga Burundi. 

Shugaban kasar Burundi Pierre Nkurunziza  da sakatare janar na majalisar dinkin duniya  Ban Ki-moon.
Shugaban kasar Burundi Pierre Nkurunziza da sakatare janar na majalisar dinkin duniya Ban Ki-moon. © REUTERS/Evrard Ngendakumana
Talla

Farhan Haq mai magana da yawun Majalisar dinkin duniya ya fadi cewa, hauhawan tarzoma da yadda ake tsare mutane ba kan gado na matukar bukatar sa ido sosai, kuma yanzu haka jamiai na sa ido sosai game da irin wainar da ake toyawa a kasar.

Hauhawan tarzomar da kama mutane ana tsarewa na zuwa ne a daidai wani lokaci da ake cika shekara guda da yunkurin da wasu sojoji suka yi na kifar da gwamnatin Pierre Nkurunziza.

Majalisar dinkin duniya na cewa, abin bukata shi ne, zama ayi sulhu a maimakon yadda ake yi tun bayan da shugaban kasar ya ayyana zarcewa da mulki da karfin tsiya.

A ranar juma'ar da ta gabata, mutane akalla 100 aka kama aka tsare su a birnin Bujumbura, a wani yunkuri na hana ‘yan adawa sakat a fadin kasar.

Ya zuwa yanzu mutane akalla 500 aka kashe yayin da wasu dubu 250 suka kaurace wa kasar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.