Isa ga babban shafi
Amurka

Amurka ta yaba da matakin Saudiya kan yaki da IS

Ma’aikatar tsaron Amurka ta yi marhaba da alwashin da Saudiya ta yi na yakar kungiyar IS ta kasa a Syria.

Sakataren tsaron Amurka, Ash Carter
Sakataren tsaron Amurka, Ash Carter REUTERS/Yuri Gripas/Files
Talla

Amurka ta dauki tsawon makwanni ta na kiran kawayanta daga kasashe 65 da ta ke jagoranta a yaki da IS a Syria da Iraqi, da su kara kaimi wajen bayar da gudun mawa, yayin da a cikin watan jiya sakataren tsaron Amurkan, Ashton Carter ya caccaki kasashen da ba su tabaka komai ba.

Mr Cater zai gana da hukumomin tsaron Saudiya a makon gobe a birnin Brussels na Belgium, inda ake sa ran tattaunawa kan tsare-tsaren kawar da kungiyar IS.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.