Wasu muhiman wuraren tarihi na fuskantar barazana
A kasar Amurka wata kungiya mai zaman kanta mai sunan Gidauniyyar kare wurare dama kayyakin tarihi ta bayana sunayen muhiman wuraren tarihi 50 dake cikin kasashe 36 a matsayin wuraren dake fuskantar barazana.
Wallafawa ranar:
Kungiyar da yanzu haka ke fatar gani Majalisar Dinkin Duniya ta maida hankali don kare kayakin tarihin daga lalacewa ko harin yan ta’ada,
Daga cikin kasashen da yanzu haka aka gano cewa wuraren tarihi su na fuskantar barazana akwai Lebanon, Jordan,Idiya,Chili, girka dama kasar Cuba.
UNESCO ta bukaci, a dai na ruguza kayayyakin tarihin da sunan yaki.
Irina ta ce akwai gine-gine a birnin Yemen, da kuma tsohon wajen ajiyar kayayyaki tarihi na Saada, da bangon tarihin Islama na Baraqish da duk hare-hare bama-bamai ya rugurguza.
UNESCO ta bayyana damuwarta dangane da yadda hare-haren suka shafi abubuwan tarihi wanda ke bada labarin asalin ‘yan kasa, da kuma hidimar da kaka da kakanni suka yi kafin zuwan Musulunci.
Tsohon Birnin Sanaa da ke cikin wasu tsaunika, Gari ne da aka kafa sama da shekaru dubu 2500, kuma ana ganinsa a matsayin cibiyar musulunci. Mai dauke da masallatai fiye da 100 da kuma wasu gidaje sama da dubu shida da aka gina tun karni na 11.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu