Isa ga babban shafi
Saudi

Ana ci gaba da neman Alhazai a Saudiya

Daruruwan Alhazai ne ake ci gaba da nema a kasar Saudiya sama da mako guda bayan tirmitsitsin da aka samu wanda ya hallaka mutane da dama.

Alhazan dai sun rasa rayukansu ne kan hanyarsu ta zuwa jifan shaidan a garin Mina.
Alhazan dai sun rasa rayukansu ne kan hanyarsu ta zuwa jifan shaidan a garin Mina. REUTERS/Directorate of the Saudi Civil Defense
Talla

Su dai hukumomin Saudiya sun bada sanarwar cewar mutane 769 ne suka mutu, yayin da wasu 934 suka samu raunuka a mummunan hadarin, ba tare da bada addin wadanda suka bata ba.

Sai dai wasu alkaluma na dabam sun nuna cewar wadanda suka mutu daga kasahse 24 sun kai 995, inda kasar Iran kawai ta ce ta rasa mutane 464, sai kuma kasar Masar da ta ce ta rasa Alhazai 124.

Najeriya ta tababtar da mutuwar alhazai 64, yayin da tace har yanzu bata ji duriyar wasu 244, yayin da kasar Mali ta rasa Alhazai 60, Indonesia 59, India 51 sai kuma Pakistan mai 46.

Jamhuriyar Nijar ta sanar da samun karin wadanda suka rasu daga 22  na adadin fako, sai Kamaru mai Alhazai 20, Chadi 11 da Ghana 8.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.