Isa ga babban shafi
Faransa

Faransa za ta gana da UAE kan rikicin Syria

Ministan tsaron Faransa Jean Yves Le Drian zai yi wata ganawa da Hadaddiyar Daular Larabawa kan yadda za’a fuskanci mayakan kungiyar ISIS a kasar Syria.

Ministan tsaron Faransa Jean-Yves Le Drian.
Ministan tsaron Faransa Jean-Yves Le Drian. AFP PHOTO / PATRICK KOVARIK
Talla

Faransa ta ce nan gaba kadan za ta kaddamar da hare haren sama kan mayakan dake da’awar jihadi wadanda ayyukansu suka dada jefa kasar cikin halin kunci.

Har ila yau tashe tashen hankulan na Syria su suka kuma haifar da dubban ‘yan gudun hijirar da yanzu haka suka kwarara zuwa Turai.

A jiya lahadi ne Le Drian ya isa Hadaddiyar Daular Larabawa kuma ana sa ran zai tabo batun rikicin Kasar Yemen a ganawar da zai yi da mahukuntan Daular.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.