Isa ga babban shafi
Amurka-Masar

John Kerry zai ganawa da shugaban Masar a yau

Sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry ya samu isowa kasar Masar, Ziyarar da za ta bashi damar ganawa da Abdel Fattah al-Sisi don duba batutuwan tsaro dama yadda za a tunkarin mayakan IS da ke da’awar Jihadi a duniya.  

John Kerry sakataren harakokin wajen Amurka
John Kerry sakataren harakokin wajen Amurka REUTERS/Andrew Harnik/Pool
Talla

A dai wajen Shugabannin za su tattauna kan batutuwan da suka shafi matsalar tattalin arziki,diflomasiya dama batutuwan kare hakin bil adam a kasar Masar.
Amurka na daya daga cikin mayan kasashe a Duniya dake bayar da gudunmuwa zuwa masar kan batutuwan da suka shafi tsaro,tareda bayar da horo zuwa dakarun Masar.
Akwai yiyuwar dai Sojojin Masar zasu kulla kawance da Amurka domin yakar Mayakan IS a Iraqi.

John Kerry bayan kasar Masar zai kai ziyara wasu kasashen Asiya dama yankin gabas ta tsakiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.