Isa ga babban shafi
Iran-IAEA

Makomar tattaunawa tsakanin Iran da manyan kasashen duniya

Sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry, ya ce yanzu lokaci ya yi da za a fahinci ko za a iya cimma yarjejeniya da kasar Iran kan shirinta na nukiliya ko kuma a’a.

Tattaunawa kan shirin nukiliyar Iran a Vienna, 25 ga watan mayun 2051.
Tattaunawa kan shirin nukiliyar Iran a Vienna, 25 ga watan mayun 2051. AFP PHOTO / POOL / SUSAN WALSH
Talla

Kerry, wanda ke zantawa da manema labarai dazun nan a birnin Vienna na kasar Austria inda kasashen duniya ke tattaunawa kan wannan batu, ya ce abu ne mai yiyuwa tattaunawar wadda za ta kawo karshe ranar 7 ga wannan wata na yuli ta haifar da sakamako nagari ko kuma akasin hakan.

A wannan lahadi wata tawaga ta manyan jami’an Hukumar Kula da Makamashin Nukiliya ta duniya IAEA, za ta isa birnin Tehran domin ganawa da manyan jami’an kasar ta Iran kan wannan batu.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.