Isa ga babban shafi
Cuba

Kotu ta daure Malaman da suka sayar da Jarabawa a Cuba

Wata kotu a kasar Cuba ta yanke hukuncin daurin shekaru takwas ga wasu Malaman Jami’a guda bakwai da aka samu da laifin sayar da jarabawar shiga Jami’a. Jaridar Granma a kasar tace Malaman sun saci takardun Jarabawar a watan Yuni tare da sayarwa akan dala 180.

RFI/Siv Channa
Talla

Ana bayar da ilimi kyauta ne a kasar Cuba, amma dole sai dalibai sun samu sakamako mai kyau kafin su shiga Jami’a.

Bayan yanke wa Malaman hukunci, kuma Kotun ta kori su daga aikin Malamanta tare da umartar su biya diyya ga Ma’aikatar ilimi da kuma Jami’ar Havana.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.