Isa ga babban shafi
China-Amurka

Mataimakin shugaban Amurka Biden ya isa China

Mataimakin Shugaban kasar Amurka, Joe Biden, ya isa kasar China, a cigaba da ziyarar kasashen dake Gabashin Asiya da ya ke yi yanzu haka, inda ake sa ran zai tattauna da hukumomin kasar.

Mataimakin shugaban kasar Amurka Joe Biden a lokacin da ya isa birnin Beijing
Mataimakin shugaban kasar Amurka Joe Biden a lokacin da ya isa birnin Beijing REUTERS/Ng Han Guan/Pool
Talla

Kafofin yada labaran China sun gargadi Biden daya kaucewa yin kalaman da zasu tada jijiyoyin wuya a kasar, kan matakin da China ta dauka na sanya wani Yanki da suke takaddama akai da Japan a matsayin na hana shawagin jiragen sama.

A lokacin da Biden ya sauka a jirgin Beijing an ganshi yana daga hannayensa a matsayin gaisuwa yayin da wasu dakaru suka tarbe shi.

Ana sa ran daga kasar ta China, mataimakin shugaban kasar zai wuce kasar Korea ta Kudu.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.