Algeria ta nemi Faransa ta amsa laifukan da ta aikata
A yau Alhamis kasar Algeria ke bukin tuna yakin da kasar ta gwabza shekaru 58 da suka gabata, domin samun ‘Yancin kai daga hannun Faransa, matakin da ya yi sanadiyar kashe daruruwan mutane. Ministan da ke kula da mazan jiyan Algeria, Mohammed Cherif Abbas, ya bukaci Faransa ta amince a hukumance kan kisan da aka yi wa ‘Yan kasar a wancan lokaci.
Wallafawa ranar:
Tuni dai shugaban Faransa, Francois Hollande, ya amince da cewa ‘Yan Sanda sun yi amfani da karfin da ya wuce kima kan masu zanga zangar neman ‘Yancin Algeria a watan Oktoban shekarar 1961.
Masana Tarihi sun ce tsakanin mutane 50 zuwa 200 ne aka kashe a lokacin yakin neman ‘Yancin kasar Algeria.
A watan Disemba ne aka sa ran shugaban kasar Faransa Francois Hollande zai kai ziyara kasar Algeria domin inganta dangata tsakanin kasashen Biyu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu