Isa ga babban shafi
Kyrgyzstan

Fadan Siyasar Da Ya Barke A Kyrgyzstan

Litinin din nan babu abin da ake gani a titunan birnin Osh na kasar Kyrgyzstan dake makwabtaka da Uzbek sai gawarwakin mutane da aka kone kurmus,yayin da mazauna yankin ke boyewa, cikin halin tsananin firgici da ake faman kone gine-gine da harbe-harbe.Kwanaki uku kena aka kwashe cur ana kafsa fada tsakanin al’umomi, wanda ya yi sanadiyyar mutane da dama, tare da yin sanadiyyar kauracewar dubunnan ‘yan kabilar UzbekA yayin da kasashen duniya ke nuna matukar damuwa da wannan tashin hankali da ya yi sanadiyyar mutuwar a kalla mutane dari da goma sha bakwai, wasu kimanin dubu suka jikkata, ‘yan kabilar Uzbek dake cewar yawan wadanda aka kashe yafi haka, sun zargi dakarun gwamnati da cewa suna taimaka wa ‘yan ta’addan Kyrgyzstan. 

Tashe-tashen hankula a Kyrgyzstan
Tashe-tashen hankula a Kyrgyzstan 路透社
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.