Isa ga babban shafi

Rikicin Iraqi: Tilas kowa ya shiga taitayinsa - MDD

Babbar jami’ar Majalisar Dinkin Duniya a Iraqi ta yi tir da rikicin da ya tashi a Iraq biyo bayan zanga – zangar kwanaki biyar da ya yi sanadin mutuwar kusan mutane 100 tare da jikkata dubbai a kasar,tana mai cewa dole a daina salawanta rayuka.

Masu zanga - zanga a Iraqi
Masu zanga - zanga a Iraqi REUTERS/Khalid al-Mousily
Talla

"kwanaki biyar na kisa da jikkata mutane bai yi ba, dole a daina," a cewar Jeanine Hennis-Plasschaert, wakiliyar babban sakaren majalisar Dinkin Duniya a Iraqi, a wani sakon tweeter da ta wallafa.

Hukumar kare hakkin dan adam ta majalisar dokokin Iraqi ta ce mutane 99 ne suka mutu, kana dubu 4 suka jikkata tun da aka fara zanga – zangar adawa da rashin ayyukan yi da rashawa a kasar.

Jami’ar Majalisar Dinkin Duniyar ta ce ta hasala da kashe – kashen da ya auku a kasar.

"Ina kira ga dukkan bangarorin da su dakata su yi karatun’ta natsu’. Ya kamata a hukunta wadanda suka haddasa wannan tarzoma. Kamata ya yi hadin kai ya samu gindin zama a Iraqi, " In ji Jeanine.

Zanga – zangar da aka fara don nuna rashin amincewa da yadda rashin aikin yi da rashawa suka yi katutu a kasar ta rikide zuwa wani gangami na neman kawo karshen rashawa tsakanin jami’en gwamnati da ma sauyin gwamnati.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.