Isa ga babban shafi
Hong Kong

Hong Kong: Masu zanga-zangar na fatan tara mutane sama miliyan 1

Dubban masu zanga-zanga a Hong Kong sun yi fitar dango kan titunan birnin, domin nunawa hukumomin yankin da kasar China gagarumin goyon bayan da suke da shi, kan aniyarsu ta neman karin 'yanci daga China, da kuma komawa kan tsarin dimokaradiya irin na Turai.

Dubban masu zanga-zangar adawa da China a yankin Hong Kong. 18/8/2019.
Dubban masu zanga-zangar adawa da China a yankin Hong Kong. 18/8/2019. Philip FONG / AFP
Talla

Zanga-zangar ta Hong Kong da ake saran za ta tara mutane sama miliyan daya, na gudana ne, duk da haramta ta da ‘yan sandan yankin suka yi, da kuma gargadin gwamnatin China.

Zuwa yanzu an shafe sama da makwanni 10 dubban masu zanga-zanga na gangami a Hong Kong, zanga-zangar da ta samo asali daga adawa da dokar mika masu laifi daga yankin zuwa China domin fuskantar hukunci.

A makon daya kare ne China ta yi tur da masu zanga-zangar a Hong Kong tare da kamanta su da ‘yan ta’adda, bayan da suka gurgunta filin jiragen saman yankin tsawon sa'o'i.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.