Isa ga babban shafi
Afghanistan

Afghanistan: IS ta dauki alhakin harin bam din da ya halaka mutane 63

Kungiyar IS ta dauki alhakin mummunan harin bam din da ya halaka mutane 63, tare da jikkata wasu 182, a wajen taron daurin aure a Kabul, babban birnin kasar Afghanistan.

Wani bangare na filin taron bikin daurin auren da aka kaiwa harin bam a Kabul, babban birnin Afghanistan.
Wani bangare na filin taron bikin daurin auren da aka kaiwa harin bam a Kabul, babban birnin Afghanistan. REUTERS/Mohammad Ismail
Talla

Kungiyar ta IS tace wani mayakinta ne ya tarwatsa bam din da ke jikinsa, yayinda ake tsaka da bikin, harin da hukumomin kasar suka ce shi ne mafi muni a baya bayan nan.

Harin ya zo ne a dai dai lokacin da wakilan mayakan kungiyar Taliban da Amurka ke gaf da cimma yarjejeniyar kawo karshen yakin kusan shekaru 18 da suke gwabzawa, matakin da zai bada damar janye dubban dakarun Amurkan dake kasar ta Afghanistan.

Tuni dai kungiyar Taliban ta nesanta kanta daga harin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.