An soke tashi da saukar jiragen sama a Hong Kong
An soke sauka da tashin jiragen sama baki daya daga a Hong Kong, sakamakon yadda masu rajin kare dimokuradiyya suka mamaye filin jirgin saman a wannan litinin.
Wallafawa ranar:
Hong Kong, a can ne ake da daya daga cikin manyan filaye jiragen sama a duniya, wanda masu tarzomar suka mamaye a daidai lokacin da suka cika makonni 10 suna zanga-zangar kin jinin shugabar gwamnatin yankin mai kwarya-kwaryan ‘yancin cin gashin kai.
Kafin tsakiyar rana, akalla mutane dubu biyar ne suka kutsa kai a cikin filin jirgin saman yayin da wasu dubbai suka yi cincirindo a waje dukanninsu dauke allunan da aka rubuta kalmomin yin tir da abin da suka kira mulkin kama karya, yayin da wasu ke jaddada kir aga shugabar gwamnatinsu ta yi marabusu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu