Zabtarewar kasa ta janyo mutuwa a China
A kasar China akalla mutane 29 ne suka rasa rayukan su bayan wata zabtarewar kasa yayinda ake ci gaba da neman wasu 22 a wani kauye mai tsaunika dake da nisan kilometa dubu 2 da dari uku da babban birnin kasar.
Wallafawa ranar:
Kasar China na daga cikin kasashe da lamarin zabtarewar kasa ke janyo mutuwar da dama daga cikin yan kasar.
A shekara ta 2017 kimanin mutane 141 suka bata sakamakon zabtarewar kasa da aka samu a kasar ta China da ya yi sanadiyar birne gidaje sama da 40 tare a wani gari dake lardin Sichuan a kudu maso yammacin kasar.
Al’amarin ya shafi yankin Sichaun, inda rahotanni suka ce zabtarewar ta janyo rusa gidaje da dama.
Gwamnatin kasar ta ware akala milyan 30 na kudin kasar a matsayin tallafi zuwa masu bincike ,kudin da za a yi amfani da su domin samarwa mutanen da suka rasa matsugunin wurin zama na gajeren lokaci.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu