Isa ga babban shafi
Korea ta Arewa-Amurka

Kim na Korea ta Arewa ya yi umarnin karfafa sashen Nukiliyar kasar

Shugaban Korea ta Arewa Kim Jong-un, ya baiwa rundunar sojin kasar, umarnin kara karfinta na harba manyan makamai masu linzami, tare da kuma bada umarnin sake gwajin wasu makaman da suka kera da suka dara na baya.

Shugaban kasar Korea ta Arewa Kim Jong Un
Shugaban kasar Korea ta Arewa Kim Jong Un 路透社。
Talla

Matakin na shugaba Kim, ya biyo bayan kama wani jirgin dakon kayan kasar da Amurka ta yi dauke makamashin kwal, bisa zarginsa da karya ka’idojin takunkuman karya tattalin arzikin da ta kakaba mata, bisa amincewar majalisar dinkin duniya.

Ana ci gaba da tayar da jijiyoyin wuya tsakanin Amurka da Korea ta Arewa, tun bayan gaza cimma matsayar da aka yi yayin tattaunawar shugaba Trump da Kim karo na biyu a birnin Hanoi na Vietnam, dangane da bukatar yin watsi shirinta na mallakar makaman Nukiliya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.