Isa ga babban shafi
Yemen

Yakin Yemen ya haifar da tagayyarar mutane mafi muni - MDD

Majalisar Dinkin Duniya, ta ce Yakin Yemen ya haifar da tagayyarar fararen hula mafi muni a duniya da aka gani a baya bayan nan.

wasu kanan Yara da yakin Yemen ya raba da muhallansu tare da haramta su ci gaba da zuwa makaranta.
wasu kanan Yara da yakin Yemen ya raba da muhallansu tare da haramta su ci gaba da zuwa makaranta. BSS/AFP
Talla

Rahoton Majalisar yace Yakin tsakanin ‘yan tawayen Houthi da dakarun wasu kasashen Larabawa a karkashin jagorancin Saudiya, ya hallaka sama da fararen hula dubu 10, yayinda wasu sama da dubu 60 suka jikkata, sai kuma akalla 'yan kasar miliyan 3 da dubu 300 da suka rasa muhallansu.

Rahoton ya kara da cewa akalla yara yan kasa da shekaru 5, miliyan da 1 dubu 800 ke fama da yunwa a kasar, bayaga wasu dubu 85 da yunwar ta hallaka a tsakanin Afrilu na 2015 zuwa Oktoban 2018.

Zalika a bangaren ilimi, sama da makarantu dubu 2 da 500 ne basa aiki, biyu bisa ukunsu kuma yakin kasar ta Yemen ne ya ragargaza su, hakan tasa kimanin kananan yara miliyan 7 ne basa zuwa makaranta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.