Isa ga babban shafi
Saudiya

Saudiya ta ki mikawa Turkiya wadanda ake zargi da kisan Kashoggi

Saudiya tace ba za ta mika ‘yan kasar domin yi musu shari’a kan kisan gillar da aka yiwa dan jarida Jamal Khashoggi a ofishin jakadancinta dake kasar Turkiya ba, kamar yadda shugaba Recep Tayyip Erdogan ya bukata.

Ministan harkokin wajen Saudiya Adel al-Jubeir.
Ministan harkokin wajen Saudiya Adel al-Jubeir. AFP/file photo
Talla

Ministan harkokin wajen Saudiya Adel al-Jubair, yace basa mika yan kasarsu zuwa wata kasa a irin wannan yanayi.

Shugaba Erdogan ya dade yana bukatar mika wadanda ake zargi domin ganin sun fuskanci shari’a amma abin yaci tura.

An hallaka Khashoggi ne ranar 2 ga watan Oktoba a ofishin Jakadancin Saudiya dake Santanbul, babban birnin Turkiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.