Saudiya
Saudiya ta ki mikawa Turkiya wadanda ake zargi da kisan Kashoggi
Saudiya tace ba za ta mika ‘yan kasar domin yi musu shari’a kan kisan gillar da aka yiwa dan jarida Jamal Khashoggi a ofishin jakadancinta dake kasar Turkiya ba, kamar yadda shugaba Recep Tayyip Erdogan ya bukata.
Wallafawa ranar:
Talla
Ministan harkokin wajen Saudiya Adel al-Jubair, yace basa mika yan kasarsu zuwa wata kasa a irin wannan yanayi.
Shugaba Erdogan ya dade yana bukatar mika wadanda ake zargi domin ganin sun fuskanci shari’a amma abin yaci tura.
An hallaka Khashoggi ne ranar 2 ga watan Oktoba a ofishin Jakadancin Saudiya dake Santanbul, babban birnin Turkiya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu