Yan gudun hijira na kwarara kasar Yemen
Majalisar Dinkin Duniya ta ce, dubban ‘yan gudun hijira na kwarara kasar Yemen duk da matsanaicin halin jinkai da kasar ke fuskanta.Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta majalisar ta ce, kimanin baki 150,000 ake sa ran su isa kasar mai fama da yakin basasa .
Wallafawa ranar:
Kakakin Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya Joel Millman, ya sheidawa manema labarai a Geneva cewar, yanzu haka kasar Yemen ta kasance babbar hanya da ‘yan gudun hijirar Afirka ke amfani don isa wadatattun kasashen yankin Gulf.
Joel ya ce, masu safarar mutane na amfana da yakin kasar wajen kaucewa shingayen binciken jami’an tsaro, don shiga kasar.
Millman ya ce, kwararan ‘yan gudun hijira zuwa Yeman zai karu da kashi hamsin, a wannan shekara, ma’ana karin dubu hamsin kan dubu 100 da suka shiga kasar a bara.
Yaki tsakanin ‘yan tawayen houti da dakarun gwamnati da ke samun goyan bayan kasashen kawance da Saudiya ke jagoranta a Yemen ya hallaka mutane da dama tare da haddasa talauci a kasar,.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu