Isa ga babban shafi
Sri Lanka

Sirisena ya maido da Majalisar Dokokin Sri Lanka bakin aiki

Shugaban Sri Lanka, Maithripala Sirisena ya janye matakinsa na dakatar da Majalisar Dokokin Kasar, yayin da ya sanya ranar Litinin mai zuwa a matsayin ranar gudanar da wata ganawa da ‘Yan Majalisun, a wani yunkuri na magance rikicin siyasar da ya kunno kai tsakanin bangarorin da ke adawa da juna.

Shugaban Sri Lanka Maithripala Sirisena
Shugaban Sri Lanka Maithripala Sirisena REUTERS/Dinuka Liyanawatte
Talla

A ranar Juma’ar da ta gabata ne, Sirisena ya nada tsohon shugaban kasa , Mahinda Rajapaksa a matsayin Firaminista bayan ya rusa gwamnatin Ranil Wickremesinghe da ya kora daga mukamin Firaminista.

A yayin jagorantar wani taro a babban birnin Colombo, Rajapaksa ya ce, shugaban kasar ya yanke shawarar dawo da Majalisar bakin aiki a ranar 5 ga wata.

Wannan matakin zai bai wa Mambobin Majalisa 225 damar zama don zaben wanda zai ci gaba da rike kujerar Firaminista tsakanin Rajapaksa da kuma Wickremensinghe .

Ana saran ‘Yan Majalisun su kada mafi yawan kuri’unsu ga wanda suke so a matsayin Firaminstan Sri Lanka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.