Taliban ta gana da manzon musamman na Amurka
Kungiyar Taliban ta tabbatar da bayanan da ke cewa wakilanta sun gana da manzon Amurka Zalmay Khalilzad a kasar Qatar inda suka tattauna dangane da yadda za a warware rikicin Afghanistan.
Wallafawa ranar:
Babbar manufa dangane da wannan ganawa da bangarorin biyu da ke hamayya da juna suka yi ita ce samar da kusance a tsakanin jami’an kungiyar ta Taliban, gwamnatin Afghanistan, Pakistan, Amurka da kuma Saudiyya, inda da ke karshen ake fatan gamsar da kungiyar domin shiga tattaunawar zaman lafiya.
Kamar yadda mai magana da yawun Taliban Zabuhullah Mujahid ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar a wannan asabar, an yi ganawar ce jiya juma’a a birnin Doha na kasar Qatar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu