Isa ga babban shafi
Syria

Putin ya bukaci kudaden sake gina Syria daga kasashen Turai

Shugaban Rasha Vladmir Putin ya bukaci kasashen turai da su bayarda gudunmawar kudaden da za’a yi amfani da su wajen sake gina kasar Syria da yaki ya dai-daita, domin baiwa miliyoyin ‘yan kasar da ke gudun hijira damar komawa gida.

Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin.
Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin. REUTERS/Sergei Karpukhin
Talla

Putin wanda yayi wannan kira gabannin ganawarsa da shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel a yau Lahadi, ya ce gudunmawar za ta taimaka wajen rage matsalar yawaitar kwarar ‘yan gudun hijirar da kasashen turai ke kokarin maganacewa.

Shugaban na Rasha ya ce a halin da ake ciki, akwai ‘yan kasar Syria akalla miliyan daya da ke gudun hijira a Jordan, sai kuma wasu ‘yan kasar ta Syria miliyan guda da ke Lebanon.

A kasar Turkiya kadai kuwa shugaba Putin ya ce yawan ‘yan Syria da ke gudun hijira a kasar ya kai miliyan uku.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.