Isa ga babban shafi
China

Wani hadari a China ya haddasa mutuwar mutane 19

Wasu mutane 19 sun mutu sakamakon wani hadari da aka samu a yankin da ake da masana’antun Sichuan dake kasar ta China.

Yankin Tianjin,daya daga cikin yankunan da aka fi samu hadura a kasar China
Yankin Tianjin,daya daga cikin yankunan da aka fi samu hadura a kasar China REUTERS/Stringer
Talla

Rahotanni sun ce an samu hadarin ne a wani kamfani wanda ya haifar da wata fashewa mai karfi kafin hayaki ya tirnike ginin.

Ya zuwa yanzu ba’a san abinda ya haifar da hadarin ba, amma hukumomi sun ce anyi nasarar kashe wutar.

A yan shekaru da suka gabata an sha samu mutuwar mutane sakamakon hadura daga Kamfanoni.

A shekara ta 2015 kusan mutane 165 ne suka mutu a yankin Tianjin dake arewacin kasar sanadiyar wuta a wata masana’antar dake yankin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.