Isa ga babban shafi
Gutterss-Rohingya

Gutteres zai ziyarci 'Yan gudun hijirar Rohingya da ke Bangladesh

Sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Gutteress zai fara wata ziyara zuwa Bangladesh tare da rakiyar shugaban bankin duniya Jim Yong Kim don nazarta bukatar dubban musulmi ‘yan kabilar Rohingya da rikici ya rabo su da Myanmar bayan kisan kiyashin da aka yi musu.

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres.
Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres. REUTERS/Mike Segar
Talla

Sanarwar da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar ta ce ziyarar ta kwanaki 2 na a matsayin nuna ban girma ga Bangladesh wadda ta taka rawar gani wajen bayar da matsugunai ga dubban ‘yan gudun hijirar tun daga bara zuwa yanzu.

Tun bayan fara kai musu hare-haren kare dangin cikin watan Agusta akalla musulmi marasa rinjaye ‘yan kabilar Rohingya daga kasar Mynamar fiye da dubu dari 7 ne su ka yi hijira zuwa makociyar kasar Bangladesh don tsira da rayukansu.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.