Isa ga babban shafi
Afghanistan-Taliban

Masu tattaki a Afghanistan don samar da zaman lafiya sun isa Kabul

Masu fafutukar samar da zaman lafiya a kasar Afghanistan wadanda suka yi tattaki na tsawon kilomita 700 a cikin kwanaki 40, a yau litinin sun isa Kabul fadar gwamnatin kasar.

Tattakin masu fafutukar ya fara ne tun kafin watan Ramadana inda su ke da fatan ganin an samu jituwa tsakanin gwamnati da kungiyar Taliban don samar da wanzajjen zaman lafiya a kasar ta Afghanistan da ke fuskantar yake-yake.
Tattakin masu fafutukar ya fara ne tun kafin watan Ramadana inda su ke da fatan ganin an samu jituwa tsakanin gwamnati da kungiyar Taliban don samar da wanzajjen zaman lafiya a kasar ta Afghanistan da ke fuskantar yake-yake. REUTERS/Mohammad Ismail
Talla

Masu tattakin sun zagaya a biranen kasar da dama a kafa a duk tsawon watan Ramadana, inda suke yi kira ga gwmanatin da kuma ‘yan Taliban da su rungumi zaman lafiya.

Sai dai kuma Isar masu faftukar birnin Kabul na zuwa a dai dai lokacin da Taliban ta yi watsi da tayin kara wa'adin tsagaita wuta tsakaninsu da Sojin kasar da kuma na hadaka.

Tun farko dai gwamnatin ce ta bukaci tsagaita wutar don gudanar da bukukuwan sallah Lafiya inda kuma daga bisani ta bukaci tsawaita wa'adin amma Taliban ta  ki.

Fatan masu faftukar bai wuce ganin an kawo karshen rikicin da ke tsakanin bangarorin biyu ba, tare da ganin an samu wanzuwar zaman lafiya a kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.