Yan Sanda sun gudanar da bincike a gidan Najib Razak
‘Yan sandan Malaysia sun kai samame kan wasu gidajen tsohon Firaministan kasar Najib Razak a Kuala Lumpur, inda suka shafe sa’oi suna gudanar da bincike akan zarge zargen karkatar da kudade da ake zarginsa da yi.
Wallafawa ranar:
A makon da ya gabata ne sabon Firaministan kasar Mahathir Muhd ya haramtawa Najib da mai dakinsa tafiya zuwa ketare har sai abinda hali yayi a binciken da yake gudana a kansa, zarge-zargen da tsohon Firaministan ya sha musantawa.
Kungiyoyin kare hakokin bil adam a kasar na bukatar gani an kare lafiyar tsohon Firaministan da mai dakinsa tareda baiwa alkalai damar gudanar da ayyukan bisa gaskiya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu