Isa ga babban shafi
Afghanistan

Taliban za ta yi tattaunar zaman lafiya da Amurka

Kungiyar Taliban ta ce a shirye take ta shiga tattaunawar zaman lafiya kai-tsaye da Amurka, da nufin samar da zaman lafiya da tsaro a kasar ta Afghanistan mai fama da hare-haren ta'addanci daga kungiyoyi daban-daban.

Hare-haren ta'addanci a kasar ta Afghanistan na ci gaba da tsananta a baya-bayan inda ko a karshen makon da ya gabata wasu munanan hare-hare 3 a jere suka hallaka fiye da mutane 20.
Hare-haren ta'addanci a kasar ta Afghanistan na ci gaba da tsananta a baya-bayan inda ko a karshen makon da ya gabata wasu munanan hare-hare 3 a jere suka hallaka fiye da mutane 20. REUTERS/Anil Usyan
Talla

Sanarwar ta Taliban na zuwa ne yayin da ya rage kwanaki kadan a fara wani taron samar da zaman lafiya a birnin Kabul, taron da ake sa ran halartar akalla wakilan kasashen duniya 25.

Sanarwar ta ce kofa a bude ta ke ga Amurkan ta tattauna kai tsaye da ofishin da ke kula da harkokin siyasa na kungiyar wadda ta kira kan ta da ''Islamic Emirate'' don samar da zaman lafiya a kasar ta Afghanistan.

A kwanakin da suka gabata ne wata manzon musamman da ga gwamnatin Amurka mai suna Alice Wells, ta ziyarci Kabul, inda ta bayyana aniyarsu ta shiga tattaunawa da kungiyar ta Taliban.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.