Isa ga babban shafi
Afghanistan

Yawan wadanda harin bam ya hallaka a Kabul ya kai 95

Kungiyar Taliban ta dauki alhakin kai harin bam da aka boye a cikin wata motar daukar marasa lafiya, da zuwa yanzu jami’an agaji a Afghanistan suka ce yawan wadanda suka hallaka a dalilinsa, ya kai akalla mutane 95, yayin da yawan wadanda suka jikkata ya kai 158.

Shingen jami'an 'yan sanda da kungiyar taliban ta kai harin a Kabul, babban birnin kasar Afghanistan. Janairu 27, 2018.
Shingen jami'an 'yan sanda da kungiyar taliban ta kai harin a Kabul, babban birnin kasar Afghanistan. Janairu 27, 2018. REUTERS/Omar Sobhani
Talla

An kai harin ne a yau Asabar a gaf da wani shingen bincike na ‘yan sandan kasar da ke kusa da ofisoshin jakadancin kasashen ketare da suka hada da na Sweden, Kungiyar tarayyar turai, da kuma India, a babban birnin kasar Kabul.

Karo na biyu kenan da Taliban ke ikirarin kai hari a birnin Kabul, bayan wanda ta kai makon da ya gabata kan wani Otal, inda suka hallaka mutane 20.

A farkon makon nan ne kuma kungiyar IS ta kai hari kan ofishin bada agaji na 'Save the Children' a birnin Jalalabad, inda ta hallaka mutane 3.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.