Isa ga babban shafi
Nepal

Nepal ta kafa dokar haramtawa mutane hawa tsaunin Everest

Gwamnatin Nepal ta haramtawa mutane hawa tsaunukan da ke kasar su kadai, ba tare da taimakon jami'ai ba, musamman ma tsauni mafi tsawo a duniya wato Everest.

Wani kwararren mai hawa tsaunuka dan kasar Japan Takako Arayama, mai shekaru 70, a lokacin da yake jagorantar wasu mahaya tsaunuka, domin kai wa saman tsauni mafi tsawo da girma a duniya, Everest. 17 ga watan Mayu, 2006.
Wani kwararren mai hawa tsaunuka dan kasar Japan Takako Arayama, mai shekaru 70, a lokacin da yake jagorantar wasu mahaya tsaunuka, domin kai wa saman tsauni mafi tsawo da girma a duniya, Everest. 17 ga watan Mayu, 2006. REUTERS/Stringer
Talla

Sabuwar dokar ta kuma haramtawa guragu, da makafi yunkurin hawa tsaunin na Everest ba tare da gabatar da shaidar takarda ta tantance lafiyarsu daga asibiti ba.

Wani jami’i a ma’aikatar bunkasa yawon bude ido a kasar ta Nepal yace an kafa sabuwar dokar ce domin rage yawan hadurra da hasarar rayukan da ake samu na daruruwan mutanen da suke yin yunkurin hawa tsaunin.

A zangon karshe na shekarar 2017, akalla mutane 6 suka hallaka, ciki harda wani dan shekara 85, mai suna min Bahadur Sherchan, wanda ya yi kokarin kare kambunsa na zama mafi yawan shekaru a duniya da ya yi nasarar kai wa kololuwar tsaunin na Everest a baya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.