Isa ga babban shafi
Iran

Iran-Masu zanga-zanga sun bijire wa gwamnati

Masu zanga-zanga a Iran sun bijire wa gargadin da gwamnati ta yi, inda suka ci gaba da fitowa a titunan ƙasar domin nuna fushin su kan matsi na tattalin arziƙi.

Mutane na zanga-zanga a Tehran babban birnin Iran bisa matsin tattalin arziki.
Mutane na zanga-zanga a Tehran babban birnin Iran bisa matsin tattalin arziki. HAMED MALEKPOUR / TASNIM NEWS / AFP
Talla

Asabar ɗinnan ce rana ta 3 da ake gudanar da zanga-zangar, inda ƴan sanda suka yi arangama da mutane masu furta kalaman nuna ƙiyayya ga gwamnati a kusa da Jami’ar birnin Tehran.

A ranar Alhamis ne zanga-zangar ta fara a Mashhad, birni na biyu mafi girma a ƙasar ta Iran.

Wasu daga cikin masu zanga-zangar sun rinƙa yin kalamai na nuna goyon baya ga masarautar da masu juyin-juya-halin musulunci suka kifar a shekarar 1979, yayin da wasu su sukar gwamnatin bisa mayar da hankali kan goyon bayan Falasɗinawa a maimakon bunƙasa tattalin arziƙin ƙasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.