Kwamitin tsaro zai fayyace matsayinsa kan Birnin Kudus
A wannan Litinin Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya zai kada kuri’a domin bayyana matsayinsa dangane da matakin da shugaban Amurka Donald Trump ya dauka, na bayyana Birnin Kudus a matsayin fadar gwamnatin Isra’ila.
Wallafawa ranar:
Bayanai na nuni da cewa, wannan kuduri zai samun amincewar sauran kasashe mambobi a kwamitin na tsaro.
Sai dai Kafin daftarin ya samu amincewar, tilas ya samu goyon bayan kasashe 9 daga cikin 15 membobi a kwamitin tsaron, ba kuma tare da hawa kujerar naki daga koda kasa guda ba, a tsakanin Amurka, Faransa, China, Rasha, ko kuma Birtaniya, masu kujerun na din din din a kwamitin.
Kasar Masar ce dai ta gabatar da daftarin da ke fatan ganin Kwamitin Tsaron na MDD, ya jaddada birnin Quds a matsayin wanda ke karkashin kulawar Majalisar, abin da ke nufin cewa matakin na Amurka ya saba wa dokokin kasa da kasa.
Tun a ranar juma’ar da ta gabata ne jami’an diflomasiyyar kasar Masar suka fara tuntubar wakilan sauran kasashe 14 mambobi a kwamitin tsaron, domin neman samun nasarar wannan yunkuri nasu, to amma akwai yiyuwar Amurka za ta iya hawan kujerar na-ki domin hana faruwar hakan.
Sai dai hawan kujerar na-ki a wannan karon mataki ne da zai iya shafar kimar kasar a siyasance.
Kimanin shekara daya da ta gabata, gwamnatin Barack Obama wadda ga al’ada ke bai wa Isra’ila kariya a duk lokacin da aka gabatar da wani kuduri da ya shafi kasar, ta zura ido sauran kasashe a kwamitin tsaron suka jefa kuri’ar da ke neman Isra’ila ta dakatar da gina gidaje a yankunan Falasdinawa da ta mamaye.
To sai dai manazarta na ganin cewa zai kasance abu mai wuya gwamnatin Donald Trump ta dauki irin wannan mataki a wannan karon.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu