Isa ga babban shafi

Fatah za ta yi zanga-zangar adawa da ziyarar Mike Pence Kudus

Kungiyar Fatah ta shugaban Falasdinu Mahmoud Abbas ta kira zanga-zanga a ziyarar da mataimakin shugaban kasar Amurka, Mike Pence ke shirin kai wa birnin Kudus a mako mai zuwa.

Shugaban Falasdinawa Mahmoud Abbas
Shugaban Falasdinawa Mahmoud Abbas REUTERS/Eduardo Munoz
Talla

Kazalika Mahmoud Abbas ya sauke ganawarsa a mataimakin shugaban Amurkar, tare da gargadin cewar kasar ba ta da gurbi ko daman jagoranci tattaunawar sulhu tsakanin Falasdinu da Isra’ila.

A makon da ya gabata Shugaba Donald Trump na Amurka ya ayyana birnin na Kudus a matsayin baban birnin Isra’ila, batun da ya janyo suka daga kasashen duniya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.