Fatah za ta yi zanga-zangar adawa da ziyarar Mike Pence Kudus
Kungiyar Fatah ta shugaban Falasdinu Mahmoud Abbas ta kira zanga-zanga a ziyarar da mataimakin shugaban kasar Amurka, Mike Pence ke shirin kai wa birnin Kudus a mako mai zuwa.
Wallafawa ranar:
Talla
Kazalika Mahmoud Abbas ya sauke ganawarsa a mataimakin shugaban Amurkar, tare da gargadin cewar kasar ba ta da gurbi ko daman jagoranci tattaunawar sulhu tsakanin Falasdinu da Isra’ila.
A makon da ya gabata Shugaba Donald Trump na Amurka ya ayyana birnin na Kudus a matsayin baban birnin Isra’ila, batun da ya janyo suka daga kasashen duniya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu