Isa ga babban shafi
Myanmar

An kashe Musulmi 6,700 a Myanmar-MSF

Kungiyar Agaji ta Medicins San Frontier ta yi zargin cewar sojojin Myanmar sun kashe ‘yan kabilar Rohingya Musulmi 6,700 a watan farko da aka fara rikicin kasar.

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana kisan da aka yi wa Rohingya a matsayin kisan kare dangi
Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana kisan da aka yi wa Rohingya a matsayin kisan kare dangi REUTERS/Adnan Abidi
Talla

Rahotan kungiyar ya ce daga cikin wadanda aka kashe harda yara kanana 730 wadanda ke kasa da shekaru 5, abinda ya sa mutane sama da 600,000 suka tsere zuwa Bangladesh domin samun mafaka.

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana kisan da aka yi wa Rohingya a matsayin kisan kare dangi, sai dai ya zuwa yanzu babu wanda aka kama domin hukunta shi.

Myanmar ba ta ce uffan kan wannan rahoto ba, amma ta sha musanta zargin musgunawa da azabtar da al'ummar Rakhine wadda ta ce rikici a yankin ya soma ne lokacin da mayaka suka kai hari kan jami'an tsaro wanda ya yi sanadi mutuwar da dama a cikin watan Agustan da ya gabata.

Sojoji sun ce alkalluman wadanda aka kashe ya kai 400, ciki hada 'yan tawayen Rohingya 376, tare da wanke dakarunta a binciken cikin gida.

Gwamnatin Myanmar dai ta datse tawagar Majalisar Dinkin Duniya daga gudanar da bincike mai sahihanci kan abin da ya faru a arewacin Rakhine, duk da matsin kasashen duniya.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.