Larabawa sun buƙaci Trump ya janye matsayarsa kan Qudus
Ministocin harkokin waje na ƙasashen Larabawa sun bukaci Donald Trump na Amurka da ya janye matakin da ya ɗauka na ayyana Qudus a matsayin babban birnin Irsa’ila.
Wallafawa ranar:
Sannan sun buƙaci ƙasashen duniya da su amince da wanzuwar ƙasar Falasɗinu tare da amincewa da gabashin birnin Qudus a matsayin fadar ƙasar.
A matsayar da suka cimma, bayan kammala wani taron gaggawa da ministocin suka yi ranar Asabar a Alƙahira, babban birnin Masar, ministocin sun ce yanzu haka Amurka ta nuna wa duniya cewa ba ta cancanci zama mai shiga tsakani ba a rikicin na Falasɗinawa da Yahudawa.
Ministocin sun yi fatali, tare da Allah-wadai da matakin na Amurka.
Matakin na Amuraka na cigaba da haifar da bore a ƙasashen na Larabawa, inda masu zanga-zanga ke nuna goyon bayan su ga yankin Falasɗinu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu