Isa ga babban shafi
Palestine

'Matsayar Trump kan Qudus ba za ta taimaka ba'

Wasu manyan kasashen Turai sun ce matsayar da Amurka ta dauka na ayyana birnin Qudus a matsayin fadar gwamnatin Isra'ila ya saba wa matsayar majalisar dinkin duniya.

A ranar Juma'a ne aka gudanar da taron gaggawa kan matakin Amurka a kan birnin Qudus.
A ranar Juma'a ne aka gudanar da taron gaggawa kan matakin Amurka a kan birnin Qudus. Reuters
Talla

Kasashen da suka bayyana haka sun hada da Burtaniya, da France, da Jamus, da Italiya, da kuma Sweden.

A cikin wata sanarwar hadin guiwa da suka bayar ta-bakin manzanninsu a majalisar dinkin duniya, jim kadan bayan kammala taron gaggawa na kwamitin tsaron majalisar, kasashen sun ce matsayar ta Amuraka ba za ta taimaka wa yunkurin samar da zaman lafiya ba a yankin na gabas ta tsakiya.

Ko a ranar Juma'a sai da matakin na Amurka ya janyo zanga-zanga a kasashen musulmai, musamman ma a yankin gabas-ta-tsakiya.

Shi dai Trump ya tabbatar da aniyar Amurka ne na mayar da ofishin jakadancin kasar Amurka zuwa birnin Qudus, tare da ayyana birnin a matsayin fadar kasar Isra'ila.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.