Isa ga babban shafi

An shigar da karar Hadaddiyar Daular Larabawa gaban kotun ICC

Wata Kungiyar kare hakkin dan Adam dake da cibiya a birnin London, ta bayyana shirin gurfanar da kasar Daular Larabawa a gaban kotun duniya, saboda zarginta da aikata laifukan yaki a kasar Yemen.

Daya daga cikin mayakan 'yan tawayen Houthi, yayin da yake sintiri a wani wuri da jiragen yaki suka kai wa hari a babban birnin kasar Yemen Sanaa. 5 ga Nuwamba, 2017.
Daya daga cikin mayakan 'yan tawayen Houthi, yayin da yake sintiri a wani wuri da jiragen yaki suka kai wa hari a babban birnin kasar Yemen Sanaa. 5 ga Nuwamba, 2017. AFP/File / MOHAMMED HUWAIS
Talla

Kungiyar mai suna Arab Organisation for Human Rights, ta zargi Daular Larabawa dake cikin kawancen kasashen dake kawance da Saudi Arabia wajen kai hari kan fararen hula.

Lauyan kungiyar Joseph Breham, yace takardun karar dake gaban kotun a Hague, sun kunshi amfani da makaman da aka haramta, da kuma daukar sojojin haya domin azabtar da mutane yayin fafata yakin.

Jami’an aikin agaji sun ce Yemen na fuskantar bala’in yunwa sakamakon yakin da tuni ya hallaka sama da mutane dubu 8,000, banda wasu mutanen 2,000 da cutar kwalara ta hallaka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.