Isa ga babban shafi
Yemen

Yara miliyan 11 ke bukatar agajin gaggawa a Yemen

Majalisar Dinkin Duniya ta ce akalla kananan yara miliyan 11 ke bukatar agajin gaggawa a kasar Yemen sakamakon halin kuncin da suka shiga saboda yakin da ake gwabzawa a kasar.

Rayuwar kananan yara na ciki barazanar a Yemen
Rayuwar kananan yara na ciki barazanar a Yemen STR / AFP
Talla

Geert Cappalaere, Daraktan kungiyar UNICEF da ke kula da Gabas ta Tsakiya da kuma Arewacin Afirka ya ce a yau kasar Yemen ce mafi muni ga rayuwar yara kanana a duniya.

Jami’in ya ce yanzu haka yara miliyan biyu ke fama da matsanancin rashin abinci mai gina jiki, yayin da suke hasashen cewar a cikin ko wadanne minitina 10 yaro guda zai mutu daga cutar da ake iya magance ta.

A karon farko a karshen mako, jirgin Majalisar Dinkin Duniya dauke da kayan agaji ya fara sauka a Sanaa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.