Isa ga babban shafi
Myanmar

An cimma yarjejeniyar mayar da kabilar Rohingya gida

Kasashen Myanmar da Bangladesh sun sanya hannu kan yarjejeniyar mayar da ‘yan kabilar Rohingya gida, wadanda suka tsere a sanadiyyar rikicin yankin Rakhine.

Jagorar Myanmar Aung San Suu Kyi.
Jagorar Myanmar Aung San Suu Kyi. AUNG HTET / AFP
Talla

Hakan na zuwa ne bayan da kasashen duniya ke cigaba da matsa lamba dangane da rikicin, wanda kasar Amurka ta bayyana a matsayin yunkurin kawar da kabilar ta Rohingya daga doron kasa.

Bayan kwashe makwanni ana ja-in-ja game da ka’idojin yarjejeniyar, kasashen biyu sun cimma matsaya, a lokacin da jagorar kasar Myanmar Aung San Suu Kyi ta gana da ministan harkokin kasashen waje na Bangladesh Mahmood Ali a babban birnin kasar na Myanmar.

A cikin wani takaitaccen bayani da ya yi wa manema labarai, Ali ya ce wannan ne matakin farko na yarjejeniyar. Sai dai ba a samu bayanai game da saurarn abubuwan da ke kunshe a cikinta ba.

Wasu daga cikin batutuwan da ba a sani ba su ne yawan ‘yangudun hijira da za a bari su koma gida da kuma tsawon lokacin da za a kwashe ana aikin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.