Isa ga babban shafi
Saudiya-Yemen

Mayakan Houthi sun dauki alhakin yunkurin kai hari Riyadh

‘Yan tawayen Houthi sun dauki alhakin makami mai linzamin da aka harba da nufin rusa filin jiragen sama na birnin Riyadh da ke Saudiya, da yammacin jiya Asabar.

Rundunar sojin saman Saudiya ta lalata makami mai linzami da mayakan Houthi suka harba zuwa birnin Riyadh daga kasar Yemen.
Rundunar sojin saman Saudiya ta lalata makami mai linzami da mayakan Houthi suka harba zuwa birnin Riyadh daga kasar Yemen. REUTERS/Ronen Zvulun
Talla

Makami mai linzamin ya shafe akalla kilomita dari 800 kafin jami’an tsaron saudiya su kakkabo shi kasa.

Wani kakakin mayakan na Houthi, ya sha alwashin cewa zasu cigaba da kai hari cikin Saudiya da makamai masu linzami, saboda yadda sojojin kasar suka yi sanadin mutuwar fararen hula a yakin da suke fafatawa da ‘yan tawayen na Houthi a kasar Yemen.

Babu wanda ya jikkata bayan kabo makamin da jami’an tsaron Saudiya suka yi kasancewar babu mutane a wurin da ya fado.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.