Isa ga babban shafi
Pakistan

An yi zanga-zangar goyon bayan Musulman Myanmar

Dubban mutane sun fito zanga-zanga a Pakistan da Malaysia a yau Juma’a domin nuna  adawa da kisan Musulmin Rohingya a Myanmar wadanda ke ci gaba da tserewa zuwa Bangladesh.

Wasu daga cikin Musulman Rohingya da ke neman mafaka a Bangladesh
Wasu daga cikin Musulman Rohingya da ke neman mafaka a Bangladesh 路透社。
Talla

Masu zanga-zangar sun fito suna daga kwali mai dauke da sakon da ke alla-wadai da shugabar gwamnatin Myanmar Aung San Suu Kyi.

Suu Kyi da ta samu lambar yabo ta zaman lafiya a duniya na ci gaba fuskantar suka kan yadda ta ki fitowa fili ta soki yadda ake kisan mutanen na Rohingya.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce sama da mutane 1000 jami’an tsaron Myanmar suka kashe, yayin da sama da dubu dari uku suka fice zuwa Bangladesh don neman mafaka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.