Isa ga babban shafi
Iran

Iran zata takaita hukuncin kisa kan laifin safarar kwayoyi

Majalisar Kasar Iran ta amince da wata doka da zata takaita aiwatar da hukuncin kisan kai, kan mutanen da aka samu da laifin safarar miyagun kwayoyi a kasar.

Majalisar Iran ta amince da dokar takaita aiwatar da hukuncin kisan kai
Majalisar Iran ta amince da dokar takaita aiwatar da hukuncin kisan kai Nazanin Tabatabaee Yazdi/TIMA via REUTERS
Talla

Ita dai sabuwar dokar ta ce mutumin da aka samu da hodar ibilis din da yawan sa ya kai kilo biyu ne zai fuskanci hukuncin kisan, sabanin yadda dokar take a yanzu.

Sabuwar dokar kuma ta ce an dage hukuncin kisa kan wanda aka samu da laifin safarar tabar wiwi daga kilo 5 zuwa kilo 50.

Kungiyar kare hakkin Bil Adama ta Amnesty International wadda ta sanya kasar Iran a matsayin kasa ta 6 a duniya da tafi aiwatar da hukuncin kisa ta yaba da sauyin.

Sabuwar dokar da ake saran kaita gaban majalisar malaman kasar da ake kira Guardian Council, zata mayar da hukuncin kisan da aka yankewa mutane 5,300 yanzu haka zuwa dauri.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.