Isa ga babban shafi
Israel-Palestine

An tsaurara matakan tsaro a zagayen masallacin Quds

Rundunar sojin Isra’ila ta tsaurara matakan tsaro kusa da Masallachin Al’Aqsa da ke birnin Quds domin magance fushin Falasdinawan da za su halarci sallar Juma’a a yau, sakamakon sabbin matakan da mahukuntan Isra’ilar suka dauka domin hana wani rukuni na jama’a zuwa kusa da masallancin.

Masu ibada a masallacin Quds
Masu ibada a masallacin Quds REUTERS/Ammar Awad
Talla

An dai share tsawon kwanaki ana zaman dar dar, sakamakon matakin rufe masallancin da Isra’ila ta dauka, yayin da a wannan juma’a ta ce mata da kuma maza wadanda shekarunsu suka wuce 50 kawai ne za a bai wa damar shiga masallancin domin yin sallah a cikinsa.

Kasashen duniya da dama ne suka yi suka dangane da wannan mataki, wanda ya haifar da tashe-tashen hankula musamman daga bangaren Falasdinawa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.