An tsaurara matakan tsaro a zagayen masallacin Quds
Rundunar sojin Isra’ila ta tsaurara matakan tsaro kusa da Masallachin Al’Aqsa da ke birnin Quds domin magance fushin Falasdinawan da za su halarci sallar Juma’a a yau, sakamakon sabbin matakan da mahukuntan Isra’ilar suka dauka domin hana wani rukuni na jama’a zuwa kusa da masallancin.
Wallafawa ranar:
An dai share tsawon kwanaki ana zaman dar dar, sakamakon matakin rufe masallancin da Isra’ila ta dauka, yayin da a wannan juma’a ta ce mata da kuma maza wadanda shekarunsu suka wuce 50 kawai ne za a bai wa damar shiga masallancin domin yin sallah a cikinsa.
Kasashen duniya da dama ne suka yi suka dangane da wannan mataki, wanda ya haifar da tashe-tashen hankula musamman daga bangaren Falasdinawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu