Isa ga babban shafi
Qatar

Iran ta aikawa Qatar da kayan abinci

Kasar Iran ta aike da manyan jiragen sama biyar cike makil da kayayyaki marmari na abinci zuwa Qatar, kwanaki bayan manyan kasashen Larabawa sun yanke hulda da ita, wanda ya yi tasiri ga harkokin sufuri da kasuwanci a tsakaninsu.

Yanke hulda da kasashen Larabawa suka yi da Qatar ya yi tasiri ga kasar
Yanke hulda da kasashen Larabawa suka yi da Qatar ya yi tasiri ga kasar REUTERS/Naseem Zeitoon
Talla

Jiragen na dauke ne da ton 90 na kayan marmari da na lambu da aka fi bukata a wanann lokaci na azumin Ramadan.

Kakakin ma’aikatar sufurin jiragen Iran Shahrokh Noushabadi ya ce za su ci gaba da kai wa Qatar daukin kayan abinci muddin akwai bukatar haka.

Kamfanin dillacin larabaran Iran na Tasnim ya ruwaito cewa akwai jiragen ruwa 3 da aka cika makil da ton 350 na kayan abinci da ke kan hanyar isa gabar Qatar ta hanyar tashar ruwan Dayyer da ke kusa da Iran.

Iran ta kuma bude hanyar jiragen samanta ga jirage 100 da za su yi hada-hada da Qatar, bayan Saudiya da Bahrain da Daular larabawa sun haramtawa jiragen kasar amfani da sararin samaniyarsu.

Matakin Iran a yanzu ya habbaka hada-hada a Qatar da kashi 17 cikin 100.

Iran ta yi kira ga Qatar da sauran kasashen Larabawa su rungumi tattaunawar sasantawa domin kawo karshen rikicin da ke tsakaninsu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.