Isa ga babban shafi
Qatar

Saudiyya ta fitar da sunayen 'yan ta'adda da ta ce Qatar na mara wa

Qatar ta yi watsi da hujjojin da Saudiyya da kawayenta suka bayar da ke bayyana jerin sunayen ‘yan ta’adda da suka ce kasar na mara wa baya a sassan duniya.

Ministan harkokin wajen Qatar, Mohammed ben Abderrahman al-Thani.
Ministan harkokin wajen Qatar, Mohammed ben Abderrahman al-Thani. KARIM JAAFAR / AFP
Talla

Sanarwar hadin-gwiwa ta kasahen Saudiyya, Bahrain, Masar, Hadaddiyar Daular Larabawa, ta bayyana jerin wasu daga cikin kungiyoyin da ake zargin cewa Qatar ce ke taimaka ma su.

To sai dai gwamnatin ta Qatar ta fitar da sanarwa da ke watsi da wannan zargi. Yanzu haka dai kasashen na Larabawa karkashin jagorancin Saudiyya, sun katse duk wata huldar diflomasiyya, ta sufuri, kasuwanci da dai sauransu da wannan karamar kasa da ke yankin tekun Fasha.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.