Afghanistan
Harin bam ya kashe mutane 21 a Afghanistan
Wasu tagwayen bama-bamai da suka tashi a kusa da ginin Majalisar Dokokin Afghanistan sun yi sanadiyyar mutuwar mutane 21a yau Talata.
Wallafawa ranar:
Talla
Wannan hari da aka kai a kusa da ginin Majalisar Dokokin da ke Kabul ya kuma jikkata mutane akalla 45.
Kungiyar Taliban dai ta amsa cewa, mayakanta ne suka kai wannan harin da nufin hallaka jami'an leken asirin kasar.
Bama-baman sun tashi ne a daidai wani lokacin da jama'a ke hada-hadar tafiya wuraren ayyukansu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu