Iran-Syria
Rouhani ya taya Assad Murna kan Aleppo
Shugaban Kasar Iran Hassan Rouhani ya taya shugaban kasar Syria Bashar al Assad murnar nasarar da ya samu wajen murkushe 'yan tawayen da suka mamaye birnin Aleppo.
Wallafawa ranar:
Talla
Yayin tattaunawar da suka yi ta waya, shugaba Rouhani ya ce nasarar kama birnin Aleppo gagarumar nasarar ce ga mutanen Syria kan 'yan ta’adda da masu goya musu baya.
Shugaba Assad ya yaba da irin goyan bayan da Iran ke ci gaba da bai wa Syria wajen murkushe 'yan Ta’addan.
Rahotanni sun ce sojojin Iran da dama ne tare da sojojin sa kai daga kasar ke taimakawa gwamnatin Syria a Yakin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu